Yan bindiga sun kashe wasu matasa biyu bayan sun karbi kudin fansa N2m a jihar Sokoto


An tattaro cewa wadanda lamarin ya shafa, Ibrahim Abubakar Rabah, ma’aikacin POS, kuma wanda ya kammala karatunsa na jami’ar Usmanu Danfodiyo ta Sokoto, an sace shi tare da wasu mutane biyu Mustapha Muhammad Rabah da Ummaru Ahmad, sama da wata guda a karamar hukumar Rabah ta jihar.

 Abokai da ‘yan uwa da suka tabbatar da faruwar lamarin a Facebook, sun ce ‘yan bindigar sun kashe Ibrahim da Mustapha, bayan sun biya kudin fansa N2m.

 Shima da yake tabbatar da faruwar lamarin a ranar Asabar, 8 ga watan Afrilu, wani Usama Lawal Rabah, ya ce ‘yan bindigar sun harbe Ummaru, amma ya tsira kuma a halin yanzu yana jinya a asibitin koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN