Type Here to Get Search Results !

Main event

Kotu ta bayar da umarni a yanka wani Zakara a Kano


Kotun Majistiri da ke gidan Murtala a Kano ta umarci wani mutum Isyaku Shu'aibu da ke unguwar Ja'en ya yanka Zakaransa. Dala FM Kano ta wallafa.

Maƙocinsa Malam Yusuf Muhammad Ja'en ne ya shigar da ƙara Kotun kan cewa Zakaran yana shiga haƙƙinsa ta hanyar hana shi barci da yawan Cara.

Amma koda aka karantowa wanda ake ƙara ya ce, gaskiya ne Zakaran na yawan yin Cara kuma zai yanka shi ne a bikin "Good Friday" don haka ya roƙi Kotun da ta sahale masa zuwa ranar.

Mai shari'a Halima Wali ta amince inda ta umarci ya killace Zakaran kuma ya yanka shi a Jumu'a mai zuwa wato ranar "Good Friday" É—in.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies