Kisan gomman mutane a Binuwai: Buhari ya dau zafi, ya bayar da umarnin gaggawa


Shugaban kasa Muhammadu Buhari, a cikin wannan mako, ya yi Allah-wadai da amfani da ta’addanci a matsayin makami wajen rigingimun kabilanci.

Ya kuma bukaci da a nemo wadanda suka aikata kisa kan wadanda ba su ji ba ba su gani ba a Binuwai, kuma a gaggauta magance yanayin tashin hankali gaba daya.

 Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa shugaban na Najeriya ya ba da wannan umarni ne a lokacin da yake yin Allah wadai da kashe-kashen da aka yi a Benue, inda aka kashe gomman mutane a unguwar Umogidi, Entekpa-Adoka a karamar hukumar Otukpo (LGA) a jihar

 Shugaban ya bukaci da a yi duk kokarin da za a kawo karshen "mummunan tashin hankali".

 Ya kuma umurci jami’an ayyukan sirri, ‘yan sanda da kwamandojin soji da su kara sanya ido a kowane fanni da kuma gaggauta magance rashin tsaro a yankunan da lamarin ya shafa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN