Type Here to Get Search Results !

Kai Tsaye: An Fara Cikon Zaben Gwamnoni a Jihohi Adamawa Da Kebbi


Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) za ta gudanar da cikon zaben gwamnoni a yau Asabar, 15 ga watan Afrilu a jihohin Adamawa da Kebbi. Wannan ya biyo bayan ayyana zaben gwamna na ranar 18 ga watan Maris da aka yi a matsayin wanda bai kammlu ba a jihohin.

Hakazalika, hukumar zaben za ta gudanar da cikon zabe na kujerun yan majalisun jiha da na tarayya 94. Legit ya wallafa.

Ku ci gaba da bibiyarmu don kawo maku yadda zaben ke gudana kai tsaye

Manyan yan takara da kallo ke kansu a cikon zaben gwamnoni

Ahmadu Fintiri

Gwamnan jihar Adamawa kuma dan takarar jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP).

Aisha Dahiru

Sanata kuma yar takarar gwamna na jam'iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Adamawa.

Nasiru Idris

Dan takarar gwamnan APC a jihar Kebbi wanda ke kan gaba kafin a ayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba.

Janar Aminu Bande

Dan takarar gwamnan PDP a jihar Kebbi. Ana sa ran zaben cikon zai zamo tsakanin Bande da Idris.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.
Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN