Hukuncin Kotu: ‘Yan sanda sun saki motoci 67, babura ga mabiya Shi’a bayan shekaru 8 da kwace su a jihar arewa


Rundunar ‘yan sandan Kaduna ta saki motoci 67, babura uku da ta kwace daga hannun wasu ‘yan Shi’a a shekarar 2015. PM News ya rahoto.

 Wannan dai ya kasance daidai da hukuncin da kotu ta yanke kan karar da aka shigar a ranar 15 ga watan Disamba 2021,

Wadanda suka shigar da kara (Mohammed-Auwal Yakubu da wasu 77) 'yan kungiyar Shi'a ne suka shigar da takardar sammaci ga Kwamishinan 'yan sanda da kuma  Babban Lauyan Jihar Kaduna.

A ranar 9 ga watan Nuwamba, 2022, Mai shari’a Amina Bello ta babbar kotun jihar Kaduna ta yanke hukunci .

Bayan samun hukuncin, an ba da umarnin kotu ga kwamishinan ‘yan sanda wanda shi ne wanda ake tuhuma na farko a shari’ar,” inji shi.

 Sai dai jami’in ‘yan sandan da ya sa ido kan sakin motocin ga masu shigar da kara, ya ki cewa komai kan lamarin, yana mai jaddada cewa ba shi da ikon yin hakan.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN