Da dumi-dumi: Buhari ya kori wata babbar ma'aikaciyar gwamnatinsa kasa da kwana 60 ya bar mulki


Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sallami Hajiya Saratu Umar a matsayin babbar sakatariyar hukumar bunkasa zuba jari ta Najeriya NIPC, nan take.

 Mista Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban kasar ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja.

 A cikin umarnin da shugaba Buhari ya ba wa Ministan Masana'antu, Ciniki da Zuba Jari, Richard Adebayo, shugaban ya kuma umurci babban Darakta a Hukumar da ya karbi ragamar aiki cikin gaggawa.

 Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa a watan Yulin 2022 Buhari ya amince da nadin Hajiya Saratu Umar a matsayin babbar sakatariyar hukumar NIPC na tsawon shekaru biyar.

 An fara nada Saratu a matsayin a watan Yulin 2014.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN