Yan sandan jihar Kano sun gano shirin shigowa da Yan daba jihar lokacin zabe


Rundunar Ƴansandan jihar Kano ta ce, ta gano shirin wasu Ƴansiyasa na shigo da ƴandaba jihar don tada hargitsi a lokacin zaɓe. Freedom radio Nigeria ta wallafa.

Rundunar ta gargaɗi ƴan siyasar da su dakatar da wannan yunƙuri domin gudun faɗa wa hannunta.

Ƴansandan sun ce, duk wanda aka samu da hannu a tarzoma zai ɗanɗana kuɗarsa.

Rundunar ta kuma nemi jama'a da su gaggauta sanar da jami'anta duk inda suka ga baƙin fuska.

Ku tara a shirin Mu Leƙa Mu Gano da ƙarfe 7 don jin cikakken labarin.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN