Yan iska dauke da makamai sun banka wuta a wata babbar Kotu a Najeriya


Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kona babbar kotun jihar da ke unguwar Owutu Edda da ke karamar hukumar Afikpo ta Kudu a jihar Ebonyi.

Intelregion ta rahoto harin wanda ya faru a daren Talata, 21 ga Maris, 2023, shi ne na farko da aka kai a duk wani cibiyoyi na jama'a a jihar Ebonyi tun bayan kammala zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun tarayya na 2023.

 Oluchi Uduma, magatakardar kotun ta tabbatar wa manema labarai harin a Owutu-Edda a safiyar Laraba.

A cewar ta, ‘yan bindigar sun mamaye kotun ne a ranar Talata, inda suka cinnawa ginin wuta.

 Bugu da kari, Uduma ta bayyana cewa ginin kotun, takardu, da sauran kayayyaki masu daraja sun kone gaba daya.

Shima shugaban karamar hukumar Afikpo ta kudu (LGA) Chima Nkama ya tabbatar da faruwar lamarin.  Ya ce an yi wa ‘yan sanda bayani.

 Hakazalika, jami’in hulda da jama’a (PRO) na rundunar ‘yan sandan jihar Ebonyi, Onome Onovwakpoyeya, ya tabbatar da faruwar harin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN