Type Here to Get Search Results !

Miye laifinsu: Gwamnan PDP ya kori dukkan masu mukaman siyasa a jiharsa bayan ya sha kaye a zabe


Gwamnan Jihar Abia da ke yankin kudu maso gabashin Najeriya, Okezie Ikpeazu ya amince da korar dukkan masu mukaman siyasa a jihar, jaridar Daily Trust ta rahoto.

Sakataren gwamnatin jihar Anambra, Barrister Chris Ezem ne ya fitar da sanarwar korar masu mukaman siyasan.

Rukunin wadanda Gwamna Ikpeazu ya sallama daga aiki

Wadanda abin ya shafa sun hada da: Mataimaka na musamman, Manyan mataimaka na musamman, Mashawarta na musamman da jami'ai na fasaha.

Wannan kari ne bisa masu mukaman siyasa da gwamnan ya kora bayan ya gaza yin nasarar cin zabe don zuwa majalisar dattawa kuma wanda ya so ya gaje shi ya sha kaye a zaben gwamna.

Ikpeazu ya umurci Akanta Janar ya biya wadanda aka kora albashin Maris
Gwamnan ya kuma umurci Akanta Janar na jihar ya tabbatar an biya albashin watan Maris ga dukkan masu mukaman siyasan da aka kora nan take.

Gwamnan ya musu godiya bisa gudunmawar da suka bada da ayyukansu ga jihar sannan ya musu fatan alheri a ayyukan da za su yi a gaba.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN