Type Here to Get Search Results !

Main event

An fara: Tinubu na bukatar addu'a, cewar Gwamna Masari, duba dalili


Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya bukaci ’yan Najeriya da su dage wajen yi wa zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu addu’a. Jaridar Aminiya ta rahoto
.

Masari ya bayyana haka ne wajen taron buda baki na musamman da aka shirya gidan gwamnatin Katsina, inda ya gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya sanya aka yi zabe lafiya.

A cewar gwamnan, zababben shugaban kasar, yana gudanar da taron addu’a na musamman duk shekara a watan Ramadan.

Ya ce: “Taron wannan shekarar an shirya shi don gode wa Allah kan nasarar da aka samu a zaben da ya gudana a fadin kasar nan.

“Ba abin da za mu yi face mu gode wa Allah kan nasarar da muka samu a Katsina da Najeriya.

“Wannan shi ne babban dalilin da ya sa muka hadu da shugabannin Addini, shugabannin gargajiya, ma’aikatan gwamnati da masu ruwa da tsaki.

“Akwai sabon shugaban kasa da aka zaba, yana bukatar addu’a, abu mafi muhimmanci shi ne mutane sun gane bayan zaben shugabanni suna kuma bukatar addu’a.”

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies