Matashi ya fara tattaki da kafa daga Birnin kebbi zuwa garin Aliero biyo bayan nassarar lashe zaben Sanata da Adamu Aliero ya yi a jihar Kebbi


Wani matashi mai suna Yusuf wanda aka fi sani da kowa naka, ya fara tattaki da kafa daga garin Birnin kebbi zuwa garin Aliero a karamar hukumar Aliero a jihar Kebbi.

Yusuf ya ce ya dau alkawari ne ga Allah cewa zai yi tattaki daga garin Birnin kebbi har zuwa garin Aliero idan har Allah ya sa Sanata Adamu Aliero ya ci zaben Sanata a 2023.

Ya kuma ce duba da irin yadda janar Aminu bande ya kawo karshen matsalar mallakar fili tsakanin al'ummar Badariya da barikin soji a garin Birnin kebbi ya sa kaunarsa ya zama wajibi a gurinsa.

Matashin ya fara tattaki ne jim kadan bayan Sallar Asuba ranar Laraba 1 ga watan Maris. Majiyar mu ta tabbbatar mana da cewa Yusuf kowa naka ya riga ya wuce garin Goru kan hanyarsa ta zuwa garin Aliero.

Ku biyo mu don karin bayani...

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN