Dattijon arziki: Tinubu ya magantu kan rashin tsaro ya ce dole a daina-kashe a Najeriya


Zababben shugaban kasar Najeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa kashe-kashen rashin hankali bai da hurumi a kasar nan. Legit ya wallafa.

Tinubu ya fadi hakan ne yayin da yake martani ne ga mummunan harin da yan bindiga suka kai kan ofishin yan sanda a karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara, jaridar The Cable ta rahoto.

A safiyar ranar Lahadi, 5 ga watan Maris ne yan bindiga suka farmaki yankin inda suka kashe shugaban yan sanda na yankin wato DPO, Kazeem Raheem, da wasu jami'an tsaro biyuu.

A cikin wata sanarwa dauke da sa hannun hadimininsa, Abdulaziz Abdulaziz, a ranar Litinin, Tinubu ya bayyana cewa ya zama dole al'ummar kasar su hada kansu don cin nasara a kan wadannan makasa.
Tinubu ya ce:

"A matsayinmu na kasa, ya zama dole mu hade don cin galaba kan wadannan makasan yan ta'addan a lokaci daya.
"Bai kamata kisan rashin hankali da zalunci irin wannan ya samu hurumi a kasarmu ba."
Tinubu ya kuma ce ya kamata ayi bincike a kan kisan hakimin Maigari a jihar Kano, wanda shine mahaifin Munir Dahiru Maigari, shugaban karamar hukumar Rimin Gado, rahoton Premium Times.

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN