Allah Mai Iko: Wata Ma'aikaciyar Lafiya Ta Rasu Tana Cikin Aiki a Yanayi Mai Ban Mamaki a Zamfara


Asmau Lawali Bungudu, Ma'aikacuyar jinya watau Nurse a Asibitin Ahmed Sani Yariman Bakura da ke Gusau, jihar Zamfara ta riga mu gidan gaskiya.

Tribune Online ta rahoto cewa Asmau ta rasu ne bayan ta yanke jiki ta faÉ—i yayin da take tsaka da aikinta a Asibitin.

Bayanai sun nuna cewa Marigayya Asma'u ta fito wurin aiki lafiya kalau da safiyar Laraba, amma awanni bayan fara aikin ranar aka tabbatar da rai ya yi halinsa.

Kakakin Asibitin, Auwal Usman, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce Asma'u na cikin aikinta kuma ta gwada hawan jinin kusan majinyata 30 kafin daga bisani ta faÉ—a wa Likita tana jin ba daÉ—i a zuciyarta.

A cewarsa, nan take bayan ta gaya wa Likita haka, ba zato aka ga ta yanke jiki ta faÉ—i, Likitoci sun yi iya bakin kokarinsu domin su ceto rayuwarta amma nan take ta rasu.

"Kwararrun Likitoci sun yi kokarin ceto rayuwarta amma nan take rai ya yi halinsa," inji PRO

Auwal Usman ya kara da shugabannin Asibitin karkashin jagorancin Dakta Usman Muhammad Shanawa, sun miƙa gawar mamaciyar hannun 'yan uwanta.

Wani É—an gidansu marigayya Asma'u ya tabbatar da cewa ta bar gida lami lafiya da safe, ta tafi Asibitin da take aiki a matsayin ma'aikaciyar jinya.

"Za'a mata Sallah jana'iza yau da misalin karfe 5:00 na yamma a kofar gidan Malam Abdurrahman da ke Magama a garin Bungudu."

Mallam Ibrahim Isa ya rasu ne a Asibitin cikin garin Kaduna da safiyar ranar Laraba 15 ga watan Maris, 2023.

A wata sanarwa da kwamifin masallacin ya fitar, ya ce za'a yi wa mamacin jana'iza bayan Sallar Azuhur.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN