Abin da ke faruwa yanzu: Jama'a na ta kansu, ana ta harbe-harbe a kusa da ofishin INEC a jihar Taraba


Jihar Taraba - An samu rikici da tashin hankali a birnin Jalingo na jihar Taraba yayin da ake ta jin karan harbe-harbe a kusa ofishin INEC da hukuma hedkwatar 'yan sanda, Daily Trust ta ruwaito.

Ba a dai tabbatar da dalilin wadannan harbe-harbe ba, amma majiya ta bayyana zargin cewa, an samu sabani ne tsakanin jami'an tsaro da ke gadin ofishin na INEC. Legit ya wallafa.

An gaggauta garkame shaguna da harkokin kasuwanci, kana an ga tituna shuru yayin da iyaye ke kokari da gaggauta dauka 'ya'yansu daga makaranta.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, ASP Usman Abdullahi bai amsa waya ba, kana bai dawo da sakon tes da majiya ta tura masa ba don jin halin da ake ciki.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN