Rikici ya barke, matasa sun kashe Hakimi, an sanya dokar hana fita a garin Lambata jihar Neja

Rikici ya barke, matasa sun kashe Hakimi, an sanya dokar hana fita a garin Lambata jihar Neja


An kashe hakimin kauyen Lambata da ke karamar hukumar Gurara a jihar Neja Mohammed Abdulsafur a wani rikici da ya barke tsakanin matasa da yammacin ranar Asabar, 14 ga watan Janairu. Shafin isyaku.com ya samo.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa Abdulsafur ya rasu ne sakamakon raunukan da wasu matasa suka yi masa da suka kai masa hari.

Gwamnatin jihar Neja ta sanya dokar hana fita a garin Lambata daga ranar Lahadi zuwa wani lokaci, saboda lamarin.

Sakataren gwamnatin jihar (SSG), Ahmed Ibrahim Matane, ya ce dokar hana fita za ta kasance daga karfe 6:00 na yamma zuwa 6:00 na safe.

Matane ya ce dokar hana fita za ta taimaka wa jami’an tsaro wajen daidaita al’amura a yankin, da ceton rayuka da tabbatar da dawo da doka da oda.

Ya kara da cewa;

"Gwamnati ta yi Allah wadai da tashe-tashen hankula da rashin bin doka da oda da aka yi a garin Lambata"

Marigayi hakimin kauyen, wanda ya yi ritaya a matsayin jami’in kula da shirin cutar kuturta da tarin fuka, ya bar mata daya da ‘ya’ya 13.

Daga ISYAKU.COM

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN