Karshen zamani: Yadda 'da ya sace mahaifinsa, ya karbi kudin fansa N2.5m


Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta kama wani mutum mai suna Issa Naigheti bisa zarginsa da yin garkuwa da mahaifinsa tare da karbar kudin fansa N2.5m.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Ajayi Okasanmi, ya ce jami’an rundunar da ke yaki da masu garkuwa da mutane na rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ne suka kama wanda ake zargin a unguwar Kambi da ke Ilorin.

An ruwaito Naigheti ya amsa laifinsa.  Okasanmi ya ce;

“Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake tuhumarsa da hada baki da wasu mutane biyu domin yin garkuwa da mahaifinsa, Bature Naigboho a yankin Igboho/Igbeti a jihar Oyo tare da karban kudin fansa N2.5m.”

Okasanmi ya kuma kara da cewa za a mayar da shari’ar zuwa jihar Oyo, inda nan ne aka aikata laifin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN