An kama wanda ya yi wa yarinya yar shekara 9 mai siyar da kunu fyade a kasuwa

An kama wanda ya yi wa yarinya yar shekara 9 mai siyar da kunu fyade a kasuwa

Illustrative picture only

Dan sanda mai bincike safeto Rachael Jacob-Osoola ranar Talata ya gawa wa Kotu a Ikeja cewa wani mutum mai suna Abdulraman Azirika, ya yi wa wata yarinya yar shekara 9 mai tallar kunu fyade.

Kamfanin dillacin labarai na Najeriya  (NAN) ya ruwaito. Yarinyar tana taimaka wa antinta siyar da kunu ne kafin aukuwar lamarin a kasuwar Mile 2 da ke birnin Ikko, watau Lagos.

Yarinyar wacce aka sakaya sunanta saboda dalilan tsaro ta gaya wa Kotu cewa yayin da Abdulrahaman ya kira ta domin ya siya kunu, sai ya tura ta cikin dakinsa ya kulle kuma ya aikata lalata da ita.

Ana ci gaba da sharia'ar a gaban Kotu.

Daga ISYAKU.COM

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN