Yanzu yanzu: Babbar Kotu a jihar Kebbi ta wanke, ta kuma sallami mutane 4 da aka gurfanar a gabanta bisa zargin kashe wani saurayi a Badariya


Babbar Kotun jihar Kebbi da ke zamanta a Gwadangaji, ranar 19 ga watan Disamba 2022, ta wanke mutane hudu da aka gurfanar a gabanta bisa zargin hada baki da kashe wani matashi mai suna Abbas a Unguwar Badariya a garin Birnin kebbi.

Bayan wanke wadanda aka gurfanar, Kotun ta kuma wanke su daga zargin hada baki da kuma kisan Abbas bisa hujjojin Sharia da suka bayyana a gaban Kotu.

Sai dai Kotu ta kama wasu mutane biyu da suka shiga gidan suka saci babur roba-roba da ya jawo takaddamar. Sakamakon haka Kotu ta daure su shekara 5 tare da tarar N100.000 kowannensu, Kuma idan suka kasa biyan kudin tarar, zasu yi zaman kaso na wasu shekaru 5.

Karin bayani na nan tafe....

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN