Yanzu yanzu: Babbar Kotu a jihar Kebbi ta wanke, ta kuma sallami mutane 4 da aka gurfanar a gabanta bisa zargin kashe wani saurayi a Badariya


Babbar Kotun jihar Kebbi da ke zamanta a Gwadangaji, ranar 19 ga watan Disamba 2022, ta wanke mutane hudu da aka gurfanar a gabanta bisa zargin hada baki da kashe wani matashi mai suna Abbas a Unguwar Badariya a garin Birnin kebbi.

Bayan wanke wadanda aka gurfanar, Kotun ta kuma wanke su daga zargin hada baki da kuma kisan Abbas bisa hujjojin Sharia da suka bayyana a gaban Kotu.

Sai dai Kotu ta kama wasu mutane biyu da suka shiga gidan suka saci babur roba-roba da ya jawo takaddamar. Sakamakon haka Kotu ta daure su shekara 5 tare da tarar N100.000 kowannensu, Kuma idan suka kasa biyan kudin tarar, zasu yi zaman kaso na wasu shekaru 5.

Karin bayani na nan tafe....

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN