Jihohin Arewa masu karfi da PDP bata taba samun nasara ba tun 1999 da damar su a zaben 2023


Najeriya ta koma kan tafarkin dimokuradiyya a shekarar 1999 sannan jam'iyyar PDP ta zama babbar jam'iyyar siyasa a kasar. Legit.ng ta wallafa.

A shekarar 2007, jam'iyyar PDP mai adawa a yanzu ta yi alfahari da kanta a matsayin babbar jam'iyyar siyasa a Afirka yayin da ta kara da cewa za ta yi mulkin Najeriya na kasa da shekaru 60.

Jam'iyyar PDP tun daga watan Mayun 2007, tana da kasa da jihohi 31 a karkashinta.  Jihohin sun hada da Adamawa, Akwa Ibom, Benue, Abia, Bayelsa, Anambra, Edo, Delta, Ebonyi, da Cross River.

Haka kuma a jerin sunayen akwai Jigawa, Ekiti, Imo, Enugu, Gombe, Nasarawa, Katsina, Kogi, Kaduna, Kebbi, Kwara, Plateau, Ogun, Oyo, Ondo, Rivers, Osun, Zamfara, Sokoto, Niger da Taraba.

Sai dai duk da karfin jam’iyyar PDP ba ta taba lashe jihohin Yobe da Borno da ke tsakiyar arewacin Najeriya ba.

Me ya sa PDP ba za ta ci Borno da Yobe ba a zaben 2023

Yobe  misali, ta samar da shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan.  Duk da cewa Lawan ya gaza samun tikitin komawa majalisar dattawa a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyar kuma ga dukkan alamu jam’iyyar APC tana fama da rikicin cikin gida a jihar amma jam’iyyar PDP ba za ta iya ikirarin cewa tana da karfi a jihar ba.

A jihar Borno, dan takarar mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar APC a zaben 2023, Kashim Shettima, dan jihar ne.

Ba za a iya tauye tarihin Shettima a jihar a matsayin gwamna da sanata ba, kuma damarsa ta lashe jihar a APC na da yawa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN