Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Sanata Rabi’u Musa Kwakwanso, ya bayyana masu yada rade-radin hadewar sa da wata jam’iyya a matsayin ‘yan siyasa da suka gaza.
Kwankwaso ya bayyana haka ne a ranar Alhamis, 8 ga watan Disamba yayin da yake zantawa da manema labarai a Abeokuta, jim kadan bayan ya yi jawabi ga mambobin jam’iyyar NNPP a sakatariyar jam’iyyar da ke babban birnin jihar, jaridar Punch ta ruwaito.
Dan takarar shugaban kasa na NNPP ya musanta cewa ya shirya hadewar jam’iyyar da sauran jam’iyyun siyasa gabanin babban zaben 2023.
NNPP za ta yi nasara a 2023, inji Kwankwaso
Da yake bayyana jita-jitar hadewar a matsayin "cikakkiyar maganar banza", Kwankwaso ya bayyana kwarin gwiwar cewa NNPP za ta yi nasara a 2023.
Yace:
“Wannan shirme ne. Ka ga mun yi imanin cewa ba mu wuce jam’iyyu uku ko hudu a kasar nan ba, amma nan da shekarar 2023 mai zuwa, da yardar Allah jam’iyyar NNPP za ta ci zabe a kasa da ma sauran matakai.
“Don haka, wadannan mutane ne da suka gaza ‘yan siyasa wadanda ba su da wani abin da za su gaya wa ’yan Najeriya face yada jita-jitar hadewar da ba dole ba.
“Haka ya riga ya tafi. Muna da 'yan takararmu. A dukkan jam’iyyu kowa na yakin neman zabe. Don haka ku yi watsi da wannan maganar banza.”