Mafarauci ya bindige manomi har Lahira a bakin rafi bisa kuskuren cewa Gada ne


Rahotanni sun bayyana cewa wani mafarauci mai suna Sunday Olubusade ya kashe wani matashi dan shekara 30 mai suna Kehinde mafarauci a garin Ondo na jihar Ondo.

An tattaro cewa wanda abin ya shafa, bayan aikin ranar, ya je wani kogi don yin wanka a lokacin da mafarauci ya harbe shi.

Wata majiyar ‘yan sanda da ta zanta da Vanguard ta ce da aka tambaye shi, wanda ake zargin ya ce yana farauta ne sai ya ga wata Gada, ya harbe ta.

"Amma daga baya, na ga wani mutum a kasa kuma na yi sauri na tafi wajen Yan sanda don ba da rahoto. Ban san abin da ya faru ba," in ji mafarauci.

Bayan 'yan mintuna kadan da faruwar lamarin, an gayyaci jami'an tsaro na 'yan sanda kuma an kai gawarsa dakin ajiye gawa.

Majiyar ‘yan sandan ta kara da cewa, “Nan da nan lamarin ya faru, an sanar da ‘yan sanda, sannan aka tattara jami’an binciken mu zuwa wurin da lamarin ya faru, sannan aka kwashe gawar zuwa dakin ajiyar gawarwaki, inda aka mika wanda ake zargin zuwa CID na jihar domin gudanar da bincike.

A halin da ake ciki dai an tsaurara matakan tsaro a garin biyo bayan wani harin ramuwar gayya daga wasu gungun mutanen da aka ce suna shirin daukar fansar mutuwar wanda aka kashe.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Funmi Odunlami, wadda ta tabbatar da faruwar lamarin, ta kara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN