Inna lillahi: Babbar mota ta murkushe mutane 12 har Lahira bayan ta kwace a wata jihar Arewa

Inna lillahi: Babbar mota ta murkushe mutum 12 har Lahira bayan ta kwace a jihar Arewa


Mutane 12 ne suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya afku a hanyar Agaie-Lapai a jihar Neja.

Hadarin ya afku ne a ranar Asabar, 17 ga watan Disamba, 2022, yayin da wata babbar mota ta rasa yadda za ta yi, ta afkawa wasu direbobin tankar da ke jira a bakin hanya, sakamakon lalacewar hanyar Agaie-Lapai.

Shugaban karamar hukumar Agaie, Ibrahim Sayuti, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadin da ta gabata, ya dora alhakin hadarin a kan lalacewar hanyar Agaie-Lapai.

A cewar shugaban karamar hukumar, hadurran sun zama ruwan dare a wannan hanyar.

“Wannan ba shi ne karo na farko da hakan ke faruwa a wannan shekara ba.  Mun samu yanayin yadda tankar mai dauke da man fetur ta yi kasala da konewa inda aka yi hasarar rayuka da dama," in ji shi.

“Haka zalika yanayin hanyar yana shafar harkokin tattalin arzikin kananan hukumomi domin ita wannan hanya ita ce hanya mafi sauki da ta hada yammacin Najeriya da jihohin Arewa”.

Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta tarayya a jihar Neja Kumar Tsukwam, ya ce hatsarin ya faru ne a bisa kuskure.

Ya tabbatar da cewa mutane 12 sun rasa rayukansu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN