An kama jami'in hulda da jama'a na ISWAP a kasuwar Kaduna

An kama jami'in hulda da jama'a na ISWAP a kasuwar Kaduna


Sojoji sun kama wani da ake zargin dan kungiyar Islamic State in West Africa Province (ISWAP) a jihar Kaduna.

Zagazola Makama, wani wallafi da ya mayar da hankali kan yankin tafkin Chadi ya ce wanda ake zargin mai suna Nasiru Mohammed, ana zarginsa da bayar da mafaka ga ‘yan ta’addan da ke tserewa daga arewa maso gabas.

Matsugunin na taimaka musu su zauna kafin a kai su wasu sansanoni a arewa maso yamma da tsakiyar kasar.

Mohammed wanda kuma ke taimakawa ‘yan ta’addan da kayan aiki yana aiki ne a reshen GSM na tsakiyar kasuwar Kaduna kafin a kama shi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN