ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta kwashe watanni 8 tana yi, duba dalili

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta kwashe watanni 8 tana yi, duba dalili


Kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta dakatar da ayyukan masana’antu na tsawon watanni takwas.

Kungiyar ta dauki matakin ne a karshen taron majalisar zartarwa ta kasa da aka gudanar a sakatariyar ASUU da ke Abuja daga daren Alhamis 13 ga watan Oktoba zuwa safiyar Juma’a 14 ga watan Oktoba.

Kungiyar ta kira taron ne domin sanin matakin da za ta dauka na gaba bayan da rassanta na Jihohi suka gana kan hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a makon jiya. Kotun dai ta umurci ASUU da ta dakatar da yajin aikin kafin a saurari daukaka karar da ta daukaka na hukuncin da ta umarci malaman da su koma bakin aiki.

ASUU dai ta shiga yajin aikin ne tun ranar 14 ga watan Fabrairun bana.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN