Ma’aikatan kafafen yada labarai, sun fi fuskantar cin mutunci a Najeriya – Gwamna Mohammed

Ma’aikatan kafafen yada labarai, sun fi fuskantar cin mutunci a Najeriya – Gwamna Mohammed


Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, a ranar Asabar din da ta gabata, ya ce ‘yan jarida da sauran masu aikin yada labarai ne suka fi fuskantar cin mutunci a Najeriya. Shafin isyaku.com ya samo.

NAN ta ruwaito cewa Mohammed ya bayyana hakan ne a Bauchi yayin da yake gabatar da sabbin motocin Toyota Hiece guda biyu ga ma’aikatan gidan jarida na gidan Gwamnati da kuma kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) a jihar.

A cewarsa, masu aikin yada labarai a kullum suna fama da takura, kalubalen tattara labarai da wasu lokutan ma ba su da albashi1.

Ya kara da cewa ‘yan jarida sun sha wahala a shiru duk da cewa sun dora madubi ga al'umma .

Mohammed, wanda ya ce ya bayar da motocin ne domin nuna cewa aikin jarida da ‘yan jarida suna da mutunci, ya kara da cewa dole ne a mutunta su tare da karfafa musu gwiwa su yi aiki yadda ya kamata don samar da yanayi mai kyau.

Ya ce dole ne a ba wa ‘yan jarida daraja ta fuskar gudunmawar da suke bayarwa ga al’umma.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN