Ma’aikatan kafafen yada labarai, sun fi fuskantar cin mutunci a Najeriya – Gwamna Mohammed

Ma’aikatan kafafen yada labarai, sun fi fuskantar cin mutunci a Najeriya – Gwamna Mohammed


Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, a ranar Asabar din da ta gabata, ya ce ‘yan jarida da sauran masu aikin yada labarai ne suka fi fuskantar cin mutunci a Najeriya. Shafin isyaku.com ya samo.

NAN ta ruwaito cewa Mohammed ya bayyana hakan ne a Bauchi yayin da yake gabatar da sabbin motocin Toyota Hiece guda biyu ga ma’aikatan gidan jarida na gidan Gwamnati da kuma kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) a jihar.

A cewarsa, masu aikin yada labarai a kullum suna fama da takura, kalubalen tattara labarai da wasu lokutan ma ba su da albashi1.

Ya kara da cewa ‘yan jarida sun sha wahala a shiru duk da cewa sun dora madubi ga al'umma .

Mohammed, wanda ya ce ya bayar da motocin ne domin nuna cewa aikin jarida da ‘yan jarida suna da mutunci, ya kara da cewa dole ne a mutunta su tare da karfafa musu gwiwa su yi aiki yadda ya kamata don samar da yanayi mai kyau.

Ya ce dole ne a ba wa ‘yan jarida daraja ta fuskar gudunmawar da suke bayarwa ga al’umma.

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN