Yadda wasu ma'aurata miji da matarsa suka mutu lokaci daya a gidansu


Wasu ma'aurata, Muhammad Umar da matarsa Sayyada Shamsiyya, sun rasu a jihar Katsina. 

Har yanzu babu cikakken bayani kan yadda lamarin ya faru, amma an tattaro cewa ma’auratan da suka yi aure a bara, an tsinci gawarsu a gidansu da ke Unguwar Rahamawa a cikin birnin Katsina da misalin karfe 5:00 na yammacin ranar Juma’a 19 ga watan Agusta, 2022. 

Makwabtan sun bayyana cewa ma’auratan ba su nuna alamun rashin lafiya ba, inda suka ce sun halarci Sallar Juma’a kafin a same su a mace. 

An yi jana’izar ma’auratan ne a safiyar ranar Asabar 20 ga watan Agusta kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN