Yadda wasu ma'aurata miji da matarsa suka mutu lokaci daya a gidansu


Wasu ma'aurata, Muhammad Umar da matarsa Sayyada Shamsiyya, sun rasu a jihar Katsina. 

Har yanzu babu cikakken bayani kan yadda lamarin ya faru, amma an tattaro cewa ma’auratan da suka yi aure a bara, an tsinci gawarsu a gidansu da ke Unguwar Rahamawa a cikin birnin Katsina da misalin karfe 5:00 na yammacin ranar Juma’a 19 ga watan Agusta, 2022. 

Makwabtan sun bayyana cewa ma’auratan ba su nuna alamun rashin lafiya ba, inda suka ce sun halarci Sallar Juma’a kafin a same su a mace. 

An yi jana’izar ma’auratan ne a safiyar ranar Asabar 20 ga watan Agusta kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN