Jaridar Punch ta ruwaito cewa lamarin ya afku ne a yammacin ranar Juma’a 5 ga watan Agusta a kusa da wata cocin sabuwar zamani, Mountain of Fire and Miracle Ministries, dake kan sabuwar titin Awolowo Road Extension, a Sapele.
An tattaro cewa mutumin ya fara cin zarafin matarsa ne bayan ya tambayi dalilin da ya sa ta bar gida zuwa coci ba tare da yin ayyukan gida da ya kamata ba da kuma shirya abincin dare.
Mutumin da ya kasa hakuri bai jira matarsa mai dauke da juna biyu ta yi mata bayani ba, sai ya buge ta kuma ya yi mata bulala da dama, lamarin da ya sa ta fadi nan take.
An ce masu wucewa da ’yan cocin sun garzaya wurin domin ceto matar. An tabbatar da mutuwar ta ne bayan da aka garzaya da ita asibitin da ke Obule.