Wasu zawarawa biyu masu suna Misis Martina Osom da Misis Rose Akom, sun sha dukan tsiya har lahira bayan da matasan al’ummar Ebbaken da ke Boje a karamar hukumar Boki ta jihar Cross River suka zarge su da laifin zama mayu. Shafin isyaku.com ya samo.
Vanguard ta rahoto cewa lamarin ya faru ne da safiyar ranar Asabar, 2 ga watan Agusta.
Wani da ya shaida lamarin da kuma surukin daya daga cikin tagogin da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce duka matan biyu mabiya darikar Katolika ne, suna dawowa ne daga ibadar asuba, a lokacin da matasan suka zarge su da kasancewa mayu.
“Sun hadu da surukata lokacin da take dawowa daga Coci. Kamar yadda ya kasance al'adarta ta yi sauko da tsaftace ta je Cocin kowace Asabar.
Matasan dai sun zarge ta ne da kasancewa Maiya, inda ta musanta zargin.
Amma suka ci gaba da yi mata dukan tsiya, suka umarce ta da ta furta cewa ita mayya ce. Amma tsananin roÆ™on da ta yi musu cewa ba ta da laifi duk basu yarda ba.” Inji shi
Ya ce dayar mai suna Misis Rose Akom, ita ma an ja ta ne domin ta hada da surukarsa kuma an yi mata azaba iri daya, inda aka umarce ta da ta amsa zargin da ake mata na cewa ita mayya ce.
Ya kara da cewa, "An daure su duka da igiya mai karfi, ana kuma dukan su a cikin ruwan sama duk rana har sai da suka mutu."
Ya ce ba a kama wadanda suka aikata laifin ba, kuma masu laifin suna tafiya cikin walwala a cikin al’umma.
"Abin da ya faru ke nan a wannan zamanin na wayewa a cikin wannan al'umma," in ji shi
Har yanzu rundunar ‘yan sandan jihar ba ta mayar da martani kan wannan lamarin ba.