An kori wata yarinya da mahaifinta daga yankin Nnobi da ke jihar Anambra bayan mahaifinta ya dinga yin lalata da ita har ta haifi ‘ya’ya biyu. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.
Ta bayyana sunanta da Sarauniya Bassey sannan ta kara da cewa sun fito daga jihar Cross River.
Yarinyar da wasu al’ummar yankin suka yi mata tambayoyi ta bayyana cewa mahaifinta ne ya tozarta ta wanda ya sanya ta zama matarsa ta hanyar rantsar da ita. Rahotanni sun ce hakan ya faru ne bayan da matansa suka bar shi.
Sarauniyar ta ci gaba da cewa, ba za ta iya bayyana dalilin da ya sa ta bar al’amarin na zumudin ya ci gaba da dadewa ba.