A ranar Juma’a ne wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano, karkashin jagorancin mai shari’a Abdullahi Liman, ta hana gwamnatin jihar Kano rancen naira biliyan 10 domin sanya na’urar daukar hoto ta Closed-Circuit Television (CCTV). Shafin isyaku.com ya samo.
Gamayyar kungiyoyi masu zaman kansu, Kano First Forum (KFF) ta shigar da kara mai dauke da kwanan wata 27 ga watan Yuni, wanda Darakta Janar na kungiyar Dakta Yusuf Isyaka-Rabiu ya shigar.
NAN ta ruwaito cewa KFF ta bakin lauyanta, karkashin jagorancin Mista Badamasi Suleiman-Gandu, ta roki kotun da ta hana Gwamna Abdullahi Ganduje na Kano rancen Naira biliyan 10.
Sauran wadanda ake kara a karar sun hada da Babban Lauyan Jihar Kano, Kwamishinan Kudi na Kano da Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano.
Sauran sun hada da Bankin Access, Ma’aikatar Kudi ta Tarayya, Ofishin Kula da Bashi da Hukumar Kula da Kudi.