Jerin shahararrun Taurari 5 da suka zama ‘Yan takaran siyasa a zaben 2023


Kiran da ake yi wa matasa na shiga siyasa zai yi aiki a zaben 2023. Jaridar nan ta Punch ta bayyana haka a wani rahoto da ta fitar a makon nan.

A wannan rahoto, an tattaro sunayen matasan taurari da suka amsa wannan kira, suka shiga siyasa, har suka samun tikitin shiga takara a zabe mai zuwa.

A nan za a samu taurari biyar da za a gwabza da su wajen neman kujerar siyasa a 2023:

1. Funke Akindele

A 2023, ‘Yar wasar Nollywood kuma mai hada fina-finai, Miss Funke Akindele za ta tsaya takarar kujerar matamakiyar gwamnan jihar Legas a jam’iyyar PDP.

Dr. Olajide Adediran wanda aka fi sani da Jandor ya dauki ‘yar wasar a matsayin abokiyar takararsa. Tun 1999 har yau, PDP ba ta taba mulkin Legas ba.

2. Banky W

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mawakin nan kuma ‘Dan fim, Bankole Wellington wanda aka fi sani da Banky W ya sake tsayawa takara a 2023, ya na neman kujerar majalisar tarayya a PDP.

Idan Banky W ya yi nasara a zaben, zai wakilci mazabar Eti Osa a majalisar wakilan tarayya.

3. Desmond Elliot

Yanzu haka Desmond Elliot ne yake rike da kujerar ‘dan majalisar dokoki na mazabar Surulere a jihar Legas, wannan karo ya sake samun tikiti a jam’iyyar APC.

Tun 2015 ‘dan wasan kwaikwayon ya zama ‘dan majalisa, akwai yiwuwar ya zarce har 2027.

4. Ned Nwoko

Ned Nwoko bai cikin matasa, amma shahararren mutum ne a Najeriya. Attajirin zai yi wa PDP takarar Sanata a mazabar Arewacin jihar Delta a zabe mai zuwa.

Mai kudin ya na auren taurariyar ‘yar wasar fim dinnan, Regina Daniels, su na da ‘ya ‘ya biyu.

5. Odi Okojie

Na karshe a jerin da Punch ta fitar shi ne Odi Okojie wanda ya samu tikitin takarar ‘dan majalisar wakilan tarayya a jihar Edo, yana so ya wakilci yankin Esan a 2023.

Odi Okojie ya yi suna, haka zalika mai dakinsa tun Mercy Johnson wanda tsohuwar ‘yar fim ce.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN