A ranar Alhamis, 28 ga watan Yuli ne hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta ta ICPC ta bayyana cewa ta gano jimillar Naira miliyan 540 a asusun wani malamin makarantar firamare na gwamnati yana karbar albashin N76,000. Kafar labarai na yanar gizo isyaku.com ya samo.
Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta kuma bayar da umarnin a kwace naira miliyan 120 na karshe da aka gano ga malamin, Roseline Egbuha da ke koyarwa a makarantar firamare ta Ozala, Abagana a jihar Anambra.
Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Azuka Ogugua ya fitar ta ce kotun da ke karkashin mai shari’a DU Okorowo ta kuma ba da umarnin a kwace motocin da aka gano Egbuha da wasu daga cikin wadanda ake zargin ta da laifin safarar kudade.
Cikakken bayanin umarnin kotu akan Egbuha da sauran su
Ogugua ya bayyana cewa kotun ta bayar da umarnin ta a ranakun 26 da 27 ga watan Yuni amma Lauyan hukumar ya samu Certified True Copy ne kawai a ranar Laraba 27 ga watan Yuli.
A cewar ICPC, umarnin kotun ya biyo bayan karar da hukumar ta shigar ne a shekarar 2021.
Kudirin ya kuma biyo bayan zargin da ake yi masa na Naira miliyan 540 da ake alakantawa da Egbuha da wasu ‘yan ta’addan da suka yi yunkurin boye kudaden a asusunta na Guaranty Trust Bank.