Da duminsa: Gwamna ya dakatar da Sarkin da ya ba shaharren shugaban 'yan bindiga sarauta


Gwamnatin jihar Zamfara ta dakatar da sabon Sarkin Birnin Yandoto na karamar hukumar Tsafe ta jihar, Aliyu Garba Marafa, bayan ya yi wa fitaccen kasurgumin shugaban 'yan bindiga, Adamu Aliero sarautar Sarkin Fulani. 

Kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, wannan na kunshe ne takardar da sakataren gwamnatin jihar, Kabiru Balarabe ya fitar kuma ya bai wa manema labarai a daren Lahadi. 

Kamar yadda takardar tace, "Ana sanar da jama'a cewa gwamnatin jihar Zamfara ta baranta kanta saga zagin nadin sarautar Sarkin Fulani wanda Sarkin Birnin 'Yandoton na karamar hukumar Tsafe yayi."

A saboda haka, mai girma gwamnan jihar Zamfara, Bello Mohammed Matawalle, ya yi umarni da dakatar da Sarkin a take.

"Kamar yadda ya dace, gwamnan ya amince da nada kwamiti domin bincikar lamarin da yasa Sarkin yayi wannan aikin.

“A halin yanzu, Alhaji Mahe Garba Marafa, wanda shi ne hakimin 'Yandoto zi cigaba da aiwatar da lamurran sarautar a masarautar."

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN