Ministan sharia Abubakar Malami ya ruwaito Ta'aziyar ban tausayi bayan rasuwar abokansa 3 a hatsarin mota


Ministan Sharia Kuma Antoni Janar na Najeriya Abubakar Malami SAN ya bayyana alhini da kidimewa bayan samun Labarin rasuwar abokansa guda uku a mumunar hatsarin mota.

Malami ya wallafa wani takaitaccen jawabin ta'aziyya a shafinsa na Facebook bayan samun Labarin rasuwar mutanen.

Ya ruwaito cewa:

"Labarin yana da ban tausayi da ban tsoro. Na firgita kuma na dimauce .

Nayi asarar abokai na tun kuruciyar mu na yaranta guda 3 a lokaci daya. Pharmacist Hussaini Abdullahi (Goro) Hon. Aliyu Tanko (Kwara) da Abubakar Abdullahi (Tsoho) da wani mutum daya. Mummunan hatsarin mota ya rutsa da su a hanyar su ta zuwa Birnin kebbi daga Abuja ba tare da sanin taron da muka yi da karfe 10 na safe na ranar 7 ga watan Yuli ke gudana a ranakun karshe na rayuwansu a doron kasa ba ne.

Inna lillhi wa Inna ilaihi rajuu

Allah ya jikan su da rahama.

ABUBAKAR MALAMI, SAN"


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN