A daidai lokacin da shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan ya zama dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben 2023, Gwamnonin da ke karkashin jam’iyyar sun dauki wani mataki mai tsauri.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito , Gwamnonin jam’iyyar APC, domin tabbatar da adalci wajen zaben fidda gwani, sun fitar da jerin sunayen ‘yan takarar da ake sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai zaba.
An tattaro cewa jerin sunayen ya ba da amsa mai kyau ga kiran da ake yi a fadin kasar na a mayar da mulki zuwa kudanci kuma saboda haka yana da karin ‘yan takara daga yankin.
Majiyar ta ruwaito tana cewa:
"Sun zabi daya daga kudu maso gabas, daya daga kudu maso kudu, uku kuma daga shiyyar kudu maso yamma kamar yadda suke cewa mulki ya koma kudu."
Jerin, wanda kuma Nigerian Tribune ta gani, yana da sunaye kamar haka:
Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo
Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Gwamna Kayode Fayemi
Rotimi Amaechi
Gwamna Dave Umahi