An hangi wasu ‘yan mata biyu suna fada kan wani mutum a Limbe da ke kudu maso yammacin Kamaru.
Rahotanni daga kasar Kamaru a ranar Juma'a, 10 ga watan Yuni, sun ce yawaitar mata masu fada saboda maza sun yi kamari a yankin.
Wani mazauni yankin kuma ganau, ya ruwaito cewa:
"'Yan matan garin Limbe ba su yi kasa a gwiwa ba wajen tozarta kansu da kuma wakiltar kansu a gasar fada da maza. A gaskiya maza suna da matukar muhimmanci ga wadannan matan." Clement Toh ne ya rubuta