Tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne a cikin wata hira da ya yi da jaridar Vanguard.
A cewarsa, wadannan rukunin mutanen basa kaunar Tinubu:
Wadanda ba za su marawa takarar shugabancin Tinubu baya ba
Ga abun da Lamido ya ce:
“Da kyau, idan yanzu gwamnonin kudu gaba daya suka ce duk za su koma APC, bari su fadi haka. Sannan sai a samu mutum kamar Amaechi a matsayin shugaban kasa, shin kuna ganin Wike zai yarda? Yanzu haka, Tinubu na shan gwagwarmaya daga wa? Yan uwansa! Afenifere basa son Tinubu kuma sun sha fadin haka a bayyane. Gwamnonin APC ma basa son Tinubu. Sun ce ya cika mamayewa kuma shi mai mulki kama karya ne. ina nufin shi dansu ne, mai zai hana su sa shi?
“Don haka, mu kasance masu gaskiya da amana a abun da muke yi. Idan kudancin Najeriya zasu hade sannan su ce “Muna son samar da shugaban kasa daga kudu, toh su rusa iyakar siyasarsu ta zama jam’iyyar siyasa daya sannan a ce, a misali, Amaechi ya zama dan takara, bana tunanin Wike zai yarda.
“Ku duba zancena, Buhari ba zai taba marawa Tinubu baya ba saboda tunanin mutumin. Ba zai taba marawa Tinubu baya ba. Mutane basu yarda dani ba kuma ku jira ku gani. A yanzu, gwamnonin APC sun hade ma Tinubu kai. Don haka batun samun namu kamar yadda kudu ke bukata…Gwamnonin APC ne farkon hadewa Tinubu.”