Da duminsa: Yan sandan jihar Sokoto sun damke matasa 3 bisa zargin mallakar miyagun ƙwayoyi da muggan makai


Rundunar yansandan jihar Sokoto ta ce ta kama wasu mutum uku bisa zargin mallakar miyagun ƙwayoyi da makamai a jihar. Shafin isyaku.com ya samo.

Wata takarda da Kakakin hukumar ya fitar wa Manema labarai ranar Alhamis 30 ga watan Yuni wanda shafin labarai na isyaku.com ya gani, (PPRO),  DSP Sanusi Abubakar, ya ce an cafke mutanen uku ne sakamakon bayanai da ayyukan sirri wajen gudanar da aikin Dan sanda. 

Ya ce an gudanar da irin wannan aikin ne domin a dakile yiwuwar yin amfani da matasa wajen horar da su domin aikata manyan laifuka musamman gabanin zabukan 2023.

ya ce wadanda aka kama sun hada da Mansur Yusuf, Bashiru Aliyu da Abdulwahid Zakari,

Ya ce an kama su ne lokacin da suke atisayen koyon yadda za su kaddamar da hargitsi da tashin hankali a cikin alummr jihar. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN