An kama Mafarauta 3 kan zargin garkuwa da mutane, duba yadda asiri ya tonu


Rundunar yan sandan Najeriya reshen Jihar Adamawa ta kama mafarauta uku da wasu kan hadin baki don garkuwa da mutane a kananan hukumomin Girei da Fufore a jihar, Daily Trust ta rahoto.

Mai magana da yawun yan sandan jihar, SP Sulaan Nguroje, cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce wadanda ake zargin:

"Auwal Muhammad mai shekara 28, Isa Umaru dan shekara 40, da Rabiu Mohammed dan shekara 19 an kama su suna addabar kauyukan Pariya Daware da Girei."

Ya kara da cewa yan sandan sun kwato babur guda daya da bindiga pistols wanda aka kera a Najeriya da wasu kayayyaki daga hannun wadanda ake zargin.


"Binciken da aka yi kawo yanzu ya nuna wadanda ake zargin sun ci amanar da aka basu na tsare rayyuka da dukiyoyin al'umma, suke yi wa masu garkuwa safarar abinci da wasu kayayyaki a yankin," in ji sanarwar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN