An cafke mutum hudu bisa zargin yin garkuwa da mutane a Sokoto


Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC ta kama wasu mutane hudu da ake zargi da yin garkuwa da mutane a jihar Sokoto.

Mista Muhammad Dada, Kwamandan NSCDC, Sokoto ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Sokoto ranar Juma’a.

Dada ya ce an samu nasarar ne bayan bayanan sirri da wasu mutane suka yi a Sokoto.

“An kama wadanda ake zargin ne da laifin yin garkuwa da mutane hudu a Tureta a ranar 22 ga Afrilu, inda aka karbi Naira miliyan 5 a matsayin kudin fansa.

Rundunar ta kuma samu nasarar cafke wadanda ake zargi da yin garkuwa da wani mutum daya a karamar hukumar Dange Shuni a ranar 16 ga Maris, inda aka karbi N900,000 a matsayin kudin fansa.

Kwamandan ya kara da cewa wadanda ake zargin suna cikin jerin sunayen wadanda ake nema ruwa a jallo, kuma tuni suka amince da aikata laifin da ake zarginsu da shi

Ya kara da cewa "A halin yanzu muna kammala bincikenmu kuma nan ba da jimawa ba za a mika wadanda ake zargin zuwa ga hukumar da ta dace domin ci gaba da shari'a.

Dada ya kuma yi kira ga jama’a da su kara jajircewa wajen tallafa wa gwamnati domin magance matsalolin tsaro a kasar nan. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN