Amaechi, Onu, Akpabio da dai sauransu ba sa dawo a matsayin Ministoci ba yayin da Buhari ya aika da sabbin sunayen Ministoci zuwa Majalisar Dattawa.


Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rubutawa Majalisar Dattawa wasika yana neman a tantance sunayen Ministoci bakwai.

Rotimi Amaechi, Ogbonnaya Onu, Godswill Akpabio da Emeka Nwajiuba wadanda duk suka yi murabus don neman takarar shugaban kasa ba za su koma Majalisar Ministocin shugaba Buhari ba kamar yadda aka tabbatar a cikin sabon jerin sunayen. 

Wadanda aka nada sune: Henry Ikechukwu – Jihar Abia, Umana Okon Umana – Jihar Akwa-Ibom; Ekuma Joseph – Jihar Ebonyi; Goodluck Nana Obia – Jihar Imo; Umar Ibrahim Yakubu – Jihar Kano; Ademola Adewole Adegorioye – Jihar Ondo; Odo Udi – Jihar Ribas.

Majalisar Dattawa, duk da haka, ba ta tsayar da ranar da za a gudanar da aikin tantancewar ba tukuna.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN