Wasu gungun birai sun kwace sukayi awon gaba da jariri dan wata daya daga hannun mahaifiyarsa yayin da take shayar da shi nono, duba abin da ya faru


Wasu gungun birai sun kashe wani jariri da suka sace shi daga hannun mahaifiyarsa a lokacin da take shayar da shi. Kafar labarai na yanar gizo isyaku.com ya tattaro.

Jaririn dan wata daya yana tare da mahaifiyarsa a wajen gidan dangi a wani kauye a Tanzaniya lokacin da abin takaici ya faru, in ji 'yan sanda. Yaron ya ji rauni a kansa da wuyansa kuma ya rasu a lokacin da ake jinyar gaggawa.

Kwamandan yankin James Manyama ya ce mutanen kauyen sun yi kokarin yin amfani da karfi a yunkurin ceto Luhaiba daga hannun biran.

Daga nan ne dabbar ta caccaki yaron tare da kashe shi, kamar yadda jaridar kasar Tanzaniya The Citizen ta ruwaito.

Mista Manyama ya ce: "Ta yi kururuwa don neman taimako, mutanen kauyen sun garzaya gidanta don taimaka mata wajen ganin an dawo da yaronta - mai suna Luhaiba Sa'id daga hannun birai.

'Lokacin da suka yi kokarin mayar da shi da karfi sai ya ji rauni a kai da kuma wuyansa.'

'Yan sanda sun bukaci 'yan kasar da su ci gaba da lura da dabbobi masu hadari.

Kwamandan ya kara da cewa: ''A lura cewa kauyen Mwamgongo yana da iyaka da dajin Gombe mai cike da dabbobi masu hadari.

'Al'amarin dabbobi na mamaye kauyuka ba bakon abu ba ne.'

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN