Gabanin zaben 2023, tsohon Gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya baiwa ‘yan Najeriya ra’ayi kan yadda za su sayar da kuri’unsu idan ‘yan siyasa suka tunkare su.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Dankwambo ya rubuta cewa;
''Kimar kuri'ar ku ta kai dala DUBU 500. Idan har za ku taba sayar da kuri'un ku, wannan ya kamata ya zama farashin ku.''