Kusan mutum 100 ne suka sayi Fom na takarar kujerar Yan Majalisar Dokokin jihar Kebbi kafin wa'adin rufe sayar da Fom na takara ranar Talata 10 ga watan Mayu.
Shafin labarai na isyaku.com ya samo cewa ba a taba samun yawan wadanda suka sayi Fom na neman takar kujerar Majalisar dokoki na jihar Kebbi ba a jam'iyar APC kamar a wannan karon.
Kakakin jam'iyar APC reshen jihar Kebbi Isah Asalafi ya ce
" Za a yi wa duk yan takara adalci".