Da Dumi: Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa ya yi murabus, ya fice PDP


Rahoton da muke samu yanzun ya nuna cewa, Sanata Enyinnaya Abaribe ya fice daga babbar jam'iyyar hamayya ta kasar nan PDP, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

Sanata Abaribe ya kuma yi murabus daga muƙaminsa na shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawan ƙasar nan.

Idan zaku iya tunawa Sanatan ya janye daga shiga zaɓen fitar da ɗan takarar gwamnan Abia na jam'iygar PDP, wanda ya gudana ranar Laraba da ta gabata, kwana biyu da suka shuɗe.

Ya tabbatar da ficewa daga PDP da kuma murabus daga kujerar shugaban marasa rinjaye a wasu wasiku daban-daban da ya aike wa shugaban PDP na gundumarsa dake karamar hukumar Obingwa, jihar Abia.

Haka nan kuma ya aike da kwafin waÉ—an nan takardu ga shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN