DA DUMI DUMI: 'Yan majalisar dokokin Kano 9 sun koma jam'iyyar NNPP


Mambobin jam’iyyar PDP tara a majalisar dokokin jihar Kano sun sauya sheka zuwa jam’iyyar New Nigeria People Party, NNPP. DailyNigerian ta ruwaito.

Kakakin Majalisar Uba Abdullahi ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a Kano ranar Juma’a.

Mista Abdullahi ya ce tuni ‘yan majalisar sun aika da wasika zuwa ga shugaban majalisar, inda suka sanar da majalisar cewa sun sauya sheka.

Mista Abdullahi ya ce wasu dalilan da ‘yan kungiyar suka bayar na da alaka da rikicin shugabanci a jam’iyyar PDP, a matakin jiha da kasa baki daya.

A cewarsa, ‘yan majalisar da abin ya shafa sun hada da Isyaku Ali Danja (Mazabar Gezawa), Umar Musa Gama (Mazabar Nassarawa), Aminu Sa’adu Ungogo (Mazabar Ungogo), Lawan Hussain Chediyar ‘Yan Gurasa (Mazabar Dala) da Tukur Muhammad (Mazabar Fagge). ).

Sauran sun hada da Mu'azzam El-Yakub (Mazabar Dawakin Kudu), Garba Shehu Fammar (Mazabar Kibiya), Abubakar Uba Galadima (Mazabar Bebeji) da Mudassir Ibrahim Zawaciki (Mazabar Kumbotso).

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN