
Yan bindiga sun yi yunkurin kashe babban dan APC bayan sun buda wa motarsa wuta da bindigogi
April 02, 2022
Comment
Honarabul Akogun Olùgbenga Omole, shugaban kwamitin labarai ne na majalisar Jihar Ondo, ya sha da kyar yayin da ‘yan bindiga suka kai masa farmaki a ranar 31 ga watan Maris. Legit ta ruwaito.
‘Yan bindiga sun kai wa Omole wanda dan majalisa ne karkashin jam’iyyar APC farmaki inda suka dinga harbin motarsa a ranar Alhamis da dare.
Wanda ya tabbatar wa TVC News, ya ce mummunan lamarin ya faru ne a Akure, babban birnin jihar.
0 Response to "Yan bindiga sun yi yunkurin kashe babban dan APC bayan sun buda wa motarsa wuta da bindigogi"
Post a Comment
Rubuta ra ayin ka