Abubakar Malami, Musulmi ne kuma Bafulatani. An haife shi ranar 17 ga watan Aprilu 1967 a garin Birnin kebbi, babban Birnin jihar Kebbi, a Arewacin Najeriya. Jaridar isyaku.com ya samo.
Ya fara karatunsa na Boko a makarantar framare na Nassarawa a garin Birnin kebbi, daga bisani ya tafi makarantar sakandare na College of art and Arabic studies. Ya sami Digirinsa na farko a Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto a 1991. Ya je makarantar koyon aikin Lauya a 1992.
Ya yi karatun Digiri na biyu a Jami'ar Maiduguri inda ya karanci Public administration a 1994. Bayan ya kammala Digiri na biyu, Malami ya kama aikin Lauya, har ya zama Lauyan Gwamnati, ya kuma rike mukamin Alkalancin Majistare a jihar Kebbi.
Malami ya zama mai ba da shawara kan harkokin shari'a na kasa a tsohuwar jam'iyar Congress for Progressive Change (CPC).
Yana cikin jiga-jigan Yan siyasa da suka kafa jam'iyar All Progressives Congress (APC) a 2013, kuma jagoran tsarin ganin sauran jam:iyyun siyasa kamar su Congress for Progressive Change (CPC), Action Congress of Nigeria (ACN) da All Nigeria Peoples Party (ANPP) sun hade waje daya a 2014,
Abubakar Malami ya tsaya takarar kujerar Gwamnan jihar Kebbi, amma ya janye wa Abubakar Atiku Bagudu kuma ya mara masa baya a karkashin jam'iyar APC lamari da ya kai Atiku Bagudu zama Gwamnan jihar kebbi.