Yadda mai gida ya lakaɗa wa matarsa mai juna biyu duka saboda abincin Sahur


Rundunar ‘yan sanda ta fara gudanar da bincike a kan zargin cin zarafin wata mata mai juna biyu da mijinta ya yi mata mai suna Taofeek Gbolagade. 

Rahotanni sun bayyana cewa Taofeek ya ci zarafin matarsa ​​a gidansu da ke Ogbere Housing Estate, Ibadan, da sanyin safiyar Talata 12 ga watan Afrilu. 

Yayin da wasu ke cewa mutumin ya ci zarafin matarsa ​​ne saboda rashin shirya Sahur (Abincin da Musulmi ke ci da Abuba lokacin Azumin watan Ramadan) a kan lokaci, wasu kuma na ganin ba wannan ne ya sa mutumin ya doke matarsa ​​ba.

An ce mutumin ya sha dukan matarsa ​​mai ciki sama da mintuna 30 kafin ta yi nasarar tserewa ta bar gidan.

Taofeek ya gudu ne bayan da ‘yan uwan ​​matar suka kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda. 

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Adewale Osifeso ya tabbatar da cewa an fara bincike kan lamarin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN