‘Yan bindiga sun sace dan sanda da wasu mutane biyu a cikin Masallaci, duba yadda ta faru


Wasu ‘yan bindiga da suka kai hari a wani Masallaci a Soyoye da ke karamar hukumar Abeokuta ta Arewa a jihar Ogun, sun yi garkuwa da wani sufeton ‘yan sanda da wasu mutane biyu masu ibada.

An yi garkuwa da dan sandan, Insifekta Kamarudeen Bello, wanda kuma shi ne Babban Limamin Masallacin kwanaki hudu bayan matarsa ​​ta haihu. 

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa masu garkuwan sun tuntubi iyalan wadanda lamarin ya shafa, inda suka bukaci a biya duk wanda aka kashe Naira miliyan biyar kudin fansa. Yanzu haka dai wadanda aka yi garkuwa da su sun samu ‘yanci bayan an biya su kudin fansa.

Majiyar ta shaida wa jaridar; 

“An tuntubi matar Insifeto Kamarudeen da lambar wayar daya daga cikin wadanda aka sace.

“Ban san ko nawa kowannen su ya biya ba, amma ina ganin sufeton ‘yan sandan ya bayar da kusan Naira 700,000 kafin a sake shi.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da sace mutanen tare da sako mutanen a ranar Lahadi. Oyeyemi, ya ce bai da masaniya ko an biya wani kudin fansa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN